✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

INEC ta fitar da jerin rumfunan zabe 124 da ta soke

INEC ta ce babu ko mutum daya da ke da rajista a rumfunan zabe 124 da ta gano a wasu jihohi 15

Kwana 10 kafin zaben shugaban kasa,  Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta fitar da jerin sunayen rumfunan zabe 124 da ta soke.

INEC ta ce ta soke rumfunan zaben bogin ne a wasu jihohi 15, saboda babu ko mutum daya da ke da rajista a cikinsu, don haka, ba za a yi zabe a nan ba a wannan karon.

Jerin sunayen rusassun rumfunan zaben da INEC ta fitar ya nuna Jihar Imo ce a kan gaba da rumfunan zabe 38 da ka soke.

Ga jerin jihohin da abin ya shafa da kuma yawan rumfunan zabensu da INEC ta soke:

  1. Imo – 38
  2. Abia – 12
  3. Borno – 12
  4. Binuwai – 10
  5. Kano – 10
  6. Kaduna – 8
  7. Anambra – 6
  8. Bauchi – 6
  9. Adamawa – 4
  10. Delta – 4
  11. Ebonyi – 4
  12. Enugu – 4
  13. Jigawa – 3
  14. Bayelsa – 2
  15. Edo – 1.

Hukumar ba ta yi yadda ta gano rumfunan ba, amma a baya, bayan kammala aikin rajistar masu zabe hukumar ta bayyana cewa ta soke rajistar masu zabe da ta gano sun yi fiye da sau daya.

A ranar 25 ga watan Fabrairu da muke ciki ne dai za a gudanar da zaben shugaban kasa na da Majalisun Tarayya, wanda bayansa da mako biyu za a gudanar da na gwamnoni da Majalisun jihohi a ranar 11 ga watan Maris, 2023.