✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kofin Afirka: ’Yan Arewa da ke cikin tawagar ’yan wasan Najeriya

A ranar Talata ce Najeriya za ta fara buga wasa a gasar.

A ranar Lahadi da ta gabata ce aka fara fafata Gasar Cin Kofin Afirka a birnin Yaounde na kasar Kamaru, inda mai masaukin baki, Kamaru ta doke Burkina Faso da ci biyu da daya a wasan farko.

A ranar Talata ce Najeriya za ta fara buga wasa a gasar, inda za ta goge raini da kasar Misra a wani da ake ganin mai zafi ne.

Wannan ya sa Aminiya ta zakulo ’yan wasan Najeriya da asalinsu ‘yan Arewa daga cikin ’yan wasan kasar da suke Kamaru a yanzu haka.

Zaidu Sanusi: Kungiyar FC Porto

Zaidu dan asalin Jihar Kebbi ne da ke wasa a kungiyar FC Porto da ke Portugal, inda yake buga baya ta gefen hagu.

Dan asalin garin Jega ne, kuma shekarunsa 24.

Zaidu Sanusi
Hoto: sportmole.co.uk

Sadiq Umar: Kungiyar UD Almeria

Sadiq dan asalin Jihar Kaduna ne da ke wasa a yanzu haka a kungiyar UD Almeria da ke rukuni na biyu na kasar Spain.

Yana cikin ’yan wasan Najeriya da suke lashe tagulla a gasar Olympic ta shekarar 2016. Shekarunsa 24.

Sadiq Umar
Hoto: owngoalnigeria

Ahmed Musa: Fatih Karagümrük

Ahmed Musa fitaccen dan wasan Najeriya da a yanzu yake wasa a kungiyar Fatih Karagümrük ta Turkiyya.

Dan asalin Jihar Kano ne da ya taso a garin Jos da ke Jihar Filato. Shi ne kyaftin din tawagar Super Eagles a yanzu haka.

Ahmed Musa

Simon Moses

Moses wanda aka fi sani da Ajala a Jihar Kaduna, dan asalin Jihar Binuwei ne da aka haifa a Jos, amma ya girma a Kaduna.

Ya fara taka leda ne a Jihar Kaduna, a barikin NDA. Yanzu haka yana wasa ne a kungiyar Nantes da ke Faransa.

Dan wasan kungiyar  Nantes, Moses Daddy Simon