✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kungiyar dalibai ta yi barazanar kawo cikas a zabukan APC da PDP

Kungiyar ta yi barazanar kawo tsaiko a zabukan fitar da gwani da APC da PDP za su yi.

Kungiyar daliban manyan makarantun Najeriya ta yi barazanar kawo cikas a zaben fidda gwani da jam’iyyar APC da PDP za su gudanar idan har ba a bude jami’o’o’in kasar nan ba.

Gabanin zaben shekarar 2023, harkokin siyasa sun kan kama a Najeriya, inda jam’iyyun siyasa ke shirin gudanar da zabukan fidda ‘yan takara a matakai daban-daban a watan Mayu, 2022.

Sai dai a wata sanarwa daga hannun shugaban kungiyar daliban, Sunday Asefon, kungiyar ta caccaki shirye-shiryen da ‘yan siyasa ke yi na samun tikitin tsayawa takara a yayin da jami’o’in kasar nan ke garkame tsawon kusan watanni uku sakamakon yajin aikin da ASUU ta tsunduma.

Shugaban, ya bayyana ‘yan siyasar Najeriya a matsayin miyagu masu son zuciya, marasa tausayi.

An jima ana kai ruwa rana tsakanin ASUU da gwamnatin tarayya kan batun cika mata wasu alkawuran da ta dauka mata, lamarin da ya sanya malaman jami’o’in tsunduma yajin aiki a lokuta mabambamta.