✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kwalejin hafsoshin soji ta NDA ta bude shafin neman gurbin karatu

NDA na sayar da fom ga masu son zama hafsoshin soji karo na 73.

Kwalejin Horas da Kananan Hafsoshin Soji ta Najeriya (NDA) da ke Kaduna, ta bude shafin sayar da fom ga dalibai masu sha’awar neman gurbin karatu a fannin aikin soji karo na 73.

Magatakardan Kwalejin, Birgediya Ayoola Aboaba ya ce an bude shafin tun a ranar 23 ga watan Janairu zuwa 24 ga watan Afrilun 2021 domin masu sha’awar samun gurbin daukan horo a fagen aikin soji.

Ya ce, “Masu sha’awar samun gurbi a Kwalejin na iya shiga shafinta na yanar gizo, rcapplications.nda.edu.ng, su zabi rukunin sayen form sannan su biya N3,500 kacal ta hanyar amfani da tsarin biyan kudi na REMITA.”

“A lura cewa wadanda suka biya kudin ta hanyar samun lambobin REMITA na ‘RRR’ da aka turo daga shafin namu kadai ne za mu karba,” a cewarsa.

Birgediya Ayoola, a cikin sanarwar ta ranar Lahadi, ya ce mata da kuma maza ’yan Najeriya da suka cancanci samun gurbin karatu a NDA na iya nema.

Magatakardan ya bukaci masu neman samun gurbin karatu a NDA da su sauke dukkanin ka’idodin da aka wallafa a shafin sannan su yi musu karatu na natsuwa.

Ya kuma ce masu neman gurbin su tabbata sun sanya kwalejin a matsayin zabinsu na farko yayin rajistar rubuta jarrabawar neman gurbin karatu a manyan makarantu ta JAMB.

Sannan kuma su tabbata sun samu mafi karancin makin da ake bukata a dukkannin kwasa-kwasai na digiri da ake gudanarwa a kwalejin.