✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mai shekara 102 na son tsayawa takarar shugabancin Najeriya

Tsohuwar ta ce tunda matasa sun gaza, ita za ta shiga a dama da ita.

Wata tsohuwa mai shekara 102 a duniya, Nonye Josephine Ezeanyaechi, wadda aka fi sani da ‘Mama Afirka’ ta ce ta shirya tsayawa takarar shugaban kasa, tunda matasa sun gaza shiga a dama da su.

Tsohuwar ta bayyana haka ne a gidan talabijin na kasa, NTA, yayin wata ziyara ta musamman da ta kai.

“Zan fito takarar shugaban kasa matukar matasa sun gaza fitowa a dama da su a siyasa.

“Idan kana da yara maza ko mata, yana da kyau ka horar da su ta yadda za su fi ka yin nasara a rayuwa,” inji ta.

Tsohuwar ‘yar asalin Karamar Hukumar Agwata a Jihar Anambra, ta kafa tarihin zama mutum mafi tsufa a Najeriya da ya ayyana kudurin tsayawa takarar shugaban kasa.

Tsohuwar, wadda ta sha gwagwarmaya a rayuwa, ta kafa kungiyoyi da dama tun daga gida har zuwa kasashen waje, wadanda suka hada da ‘Nigerians Diaspora Organization (Egbe Oma).

Da ya ke nasa jawabin Darakta-Janar na gidan talabijin na NTA, Yakubu Ibn Mohammed, ya jinjina wa tsohuwar kan irin rawar da ta taka a rayuwar mutane daban-daban a kasar nan.

Daraktan ya bayyana ‘Mama Afrika’ a matsayin jigo wadda Najeriya ke bukatar mutane irinta.