✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mu ɗore da kyawawan halayen da muka koya a Ramadan — Murtala Garo

Ya buƙaci 'yan Najeriya su dage da addu'a domin daidaituwar al'mura a ƙasar nan.

Ɗan takarar Mataimakin Gwamna na jam’iyyar APC a zaɓen 2023 a Jihar Kano, Murtala Sule Garo, ya yi wa ɗaukacin al’ummar Musulmi barka da sallah tare da buƙatar su ɗore da kyawawan halayen da suka koya a Ramadan.

A wani saƙon taya murna, ya ce bikin sallar bai taƙaita ga kammala azumin wajibi na watan Ramadan ba, ya haɗa da faɗakarwa da tunatarwa a tsakanin al’umma don ganin an samu zaman lafiya da arziƙi mai ɗorewa a JIhar Kano da ƙasa baki ɗaya.

“Ina taya ɗaukacin al’ummar Musulmi musamman na Jihar Kano barka da sallah.

“Muna godiya ga Allah Maɗaukakin Sarki da ya ba mu ikon azumtar watan Ramadan. Allah Ya karbi ibadunmu, ya yafe mana kurakuranmu, ya kuma ƙara ara mana lokaci nan gaba.

“Ina kira ga al’umma Musulmi da su yi amfani da darusan da muka koya cikin wannan wata mai alfarma don tabbatar da zama lafiya da ƙaunar juna a jiharmu da kuma ƙasa baki ɗaya.”

Garo, ya ce tabbas ‘yan Najeriya na fuskantar matsin rayuwa sakamakon tabarbarewar tattalin arziki, sai dai ya ce akwai buƙatar a dage da addu’a domin samun sauƙi.

“Tabbas ‘yan Najeriya na cikin wani mawuyacin hali sakamakon taɓarɓarewar tattalin arziƙi.

“Amma duk da haka ba mu cire ƙauna ga kasarmu ba. Don haka wannan lokaci wata dama ce a gare mu da za mu ci gaba da addu’o’i Allah Ya kawo mana mafita da arziƙi mai ɗorewa.”