✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mutum 8 mayakan ISWAP suka kashe a Chibok

Sun kone wasu kurmus kuma har yanzu akwai mutanen da ba a san inda suke ba.

Mayakan ISWAP sun kashe fararen hula takwas a sabon harin da kungiyar ta kai kauyen Kautakari da ke Karamar Hukumar Chibok ta Jihar Borno.

Ranar Talata da almuru ne dai mayakan ISWAP suka fara wa kauyen suna luguden wuta kan mai uwa da wabi suna banka wa gidaje wuta.

Majiyarmu a ce “Mun tsinci gawarwarki takwas daga wurin da aka kai harin jiya (Talata) a kauyen (Kautikari), amma har yanzu akwai dimbin mutane da ba a san inda suke ba.”

Majiyar ta bayyana cewa mutum takwas din da suka rasu sun hada da wasu biyu da mayakan suka kona kurmus, sai kuma wasu shida da aka tsinci gawarsu a cikin daji bayan harin.
Ta kara da cewa, “Karamin sansanin sjoijn da ke wurin ma an kona shi kurmus tare da wasu gidajen mutane”.

Mayakan na ISWAP sun kai harin ne sa’o’i kadan bayan ziyarar farko da Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres ya kai Jihar Borno.

A lokacin ziyarar da ya kai birnin Maiduguri, Guterres ya yi alkawarin bayar da gudummawa wajen ganin ayyukan ta’addanci sun zama tarihi a yankin Arewa maso Gabashin Najeriya.