✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

NAJERIYA A YAU: 2023: Yadda Tinubu Ya Karbi Batun Takarar Osibanjo

Tsakanin Tinubu da Osinbajo wa zai samu goyon bayan Fadar Shugaban Kasa?

More Podcasts

Domin sauke shirin latsa nan

Hankalin ’yan Najeriya ya koma kan yadda Uban Jam’iyyar APC na Kasa, Bola Ahmed Tinubu, da ke neman takarar shugaban kasa ya ji da fitowar Mataimakin Shugaban Kasa, Farfesa Yemi Osibanjo, takarar kujerar.

Da wace fuska Tinubun ya karbi aniyar ta Osibanjo, wanda ake kallo a matsayin  yaron gidansa? Shin wuyan Osinbajo ya kai yanka? Wadanne kalubale takarar tasa take tattare da su? Sannan tsakanin shi da Tinubu wa zai dagula wa wani lissafi?

Shirin Najeriya A Yau na wannan na tafe gamsassun bayanai.