✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ramadan: Masu karamin karfi 750 sun sami tallafin abincin azumi a Kano

Mutum 750 ne suka rabauta da tallafin

Wata kungiya mai zaman kanta a Jihar Kano mai suna NUSAID tare da hadin gwiwar Zauren Hadin Kan Malaman Kano a ranar Lahadi ta raba kayan abinci da kudi a matsayin tallafin azumi ga mutum 750 a Kano.

Mutanen, wadanda suka hada da mata da marayu da sauran masu karamin karfi dai sun rabauta da kayan  ne a wani bangare na tallafin da kungiyar ta saba bayarwa kowacce shekara a watan azumi.

A cewar mai kula da tsare-tsare na kungiyar, Dokta Sa’idu Ahmad Dukawa, sun raba kayan tallafin ne domin su rage radadin rayuwa ga mabukata musamman a watan azumi.

Ya ce, “Wannan ta jima tana bayar da tallafi a kowanne watan azumi da kuma duk lokacin da bukatar hakan ta taso tun shekara ta 2016, kamar lokacin da aka fuskanci iftila’in ambaliya a Jihohin Kano da Katsina da Jigawa a bara.

“Mutum 750 ne suka rabauta da wannan tallafin a yau, kuma abin da ke ciki kayan abinci ne sai ’yan kudin mota. A cikin kowanne kunshi akwai shinkafa da taliya da kafi-zabo da man gyada da dabino da sukari da kuma gishiri.

“Babbar manufarmu ta yin wannan aikin alherin ita ce ta rage wa masu azumi radadin halin da suke ciki, musamman a wannan watan na azumi,” in ji Dokta Dukawa.

Wasu daga cikin wadanda suka amfana da tallafin bayyana farin cikinsu musamman kasancewarsa a watan azumi, inda suka bukaci sauran kungiyoyi da sauran masu hannu da shuni da su yi koyi da kungiyar.