✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Sace Dalibai: Masu zanga-zanga na dandazo a Daura

An fara zanga-zangar #BringBackOurBoys don neman sako Daliban Kankara

Kungiyar Al’ummar Arewa (CNG) ta yi wa Jihar Katsina tsine domin zanga-zangar sai-baba-ta-gani kan garkuwa da aka yi da daliban Makarantar Sakandaren GSSS Kankara.

A safiyar Alhamis ne dandazon ’yan kungiyar ke fara macin gangamin da aka yi wa taken #BringBackOurBoys; daga nan za su isa Daura, mahaifar Shugaban Kasa Buhari, inda yake hutu.

“Babu tunani ga duk dan Arewan da zai zauna yana kallo an bar ’yan bindiga da ’yan ina-da-kisa da masu garkuwa da mutane na abin da suka ga dama a Arewa, duk da muhimmancin yankin a kasa,” inji kungiyar.

A ranar da Buhari ya sauka a Daura ne aka yi garkuwa da daruruwan daliban GSSS Kankara, a Jihar Katsina mai fama da ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane.

Mun kawo rahoton yadda wasu ’yan daba suka tarwatsa taron da CNG ta shirya a Kaduna ranar Litinin, kan matsalar tsaro da ke addabar Arewa da ma Najeriya.

Kakakin kungiyar, Abdul-Azeez Suleiman ya ce harin ba zai hana ta yin kira da a sako daliban “da sauri, a raye kuma ba da lahani ba.”

Suleiman ya ce CNG na sane cewa an jibge ’yan sanda a Jihar Katsina, don haka ya yi kira da a guji hana halastacciyar zanga-zangar da ya ce za ta gudana cikin lumana.