Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III ya tabbatar da ganin jinjirin watan Shawwal a Najeriya.
Hakan ya tabbatar da ranar Juma’a, 1 ga watan Shawwal ta shekarar 1444 Bayan Hijira a matsayin ranar Idin Sallah karama.
Sarkin, wanda kuma shi ne Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci a Najeriya (NSCIA) ya ce an tabbatar da sahihancin ganin watan a wurare da dama a fadin kasar.
Ya bukaci musulmi da su ci gaba da kasancewa jakadu na zaman lafiya da kowa ba tare da nuna wani bambanci a tsakanin al’umma ba.
Ya yi addu’ar Allah Ya yi riko da hannayen sabbin shugabanni Ya kuma albarkaci kasar baki daya.