Hukumomin Saudiyya sun gargadi al’ummar musulmi kan yaduwar ruwan ZamZam na jabu a wasu sassa na duniya.
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da hukumomin kasar ke kokarin daukar matakan magance yaduwar ruwan ZamZam na jabu da aka gani a wasu kasashen duniya.
- El-Rufai ya haramta zanga-zanga a Kaduna saboda batancin da aka yi a Sakkwato
- Mutumin da ya yi garkuwa da yaro a Kano zai bakunci hauni
Shafin Haramain da ke dandalin Twitter na hukumomin da ke kula da Masallatai Biyu Masu Daraja na Saudiyya sun wallafa hotunan robobin ruwan ZamZam na gaskiya domin ankarar da al’umma.
“Sakamakon rahotannin da ake samu na gurbataccen ruwan ZamZam a sassa daban-daban na duniya da suka hada da Birtaniya da Afirka da kuma Australia.
“Wadannan su ne hotunan robobin ruwan ZamZam na gaskiya ba na jabu ba,” a cewar sanarwar.