✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Tinubu: Bayani kan dan takarar shugaban kasar APC a 2023

Ya lashe zaben dan takarar APC bayan ya lashe fiye da rabin kuri'un da aka jefa

Dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar APC, Bola Ahmed Adekunle Tinubu, an haife shi ne a ranar 29 ga Maris, 1952.

Fitacce dan siyasar mai fada a ji a shiyyar Kudu maso Yammacin Najerya, shi ne tsohon gwamnan Jihar Legas, kuma masani ne kan hada-hadar kudi.

Tinubu ya yi karatunsa ne a Kasar Amurka, kuma ya yi aiki na wasu shekaru a kasar waje kafin dawowa gida Najeriya a shekarun 1980, inda ya ci gaba da aiki sannan daga bisani ya shiga harkar siyasa.

Ya zama Sanata mai wakiltar Mazabar Legas ta Yamma a Majalisar Dattawa a shekarar 1992 karkashin Jam’iyyar SDP.

Duk da matsin lamba ya tilasta wa Tinubu gudun hijira a 1994, daga bisani ya dawo gida bayan rasuwar Marigayi Shugaba Abacha a 1998 inda Jamhuriya ta Hudu ta kankama.

Bayan da Marigayi Sani Abacha ya rushe ‘Yan Majalisar Dattawa a 1993, Tinubu ya zama dan gwagwarmaya mai rajin dawo da tsarin mulkin dimokuradiyya.

Ya mulki Jihar Legas a matsayin gwamna na wa’adi biyu (shekara takwas), kuma a karkashin Jami’iyyar AD daga 1999 zuwa 2007.

Bayan nan, Tinubu ya ci gaba da zama fitaccen dan siyasa mai tasiri a Najeriya, wanda hakan ya ba shi damar taka muhimmiyar rawa wajen kafa jami’iyyar APC a 2013 inda ake ta damawa da shi har zuwa wannan lokaci.

A watan Janairun 2022 ne dan siyasar ya bayyana aniyarsa ta zawarcin shugabancin Najeriya a shekarar 2023.

A matsayinsa na daya daga cikin ’yan takarar Shugaban Kasa, Tinubu ya nuna wa jam’iyyarsa ta APC cewa yanzu lokaci ne da ya kamata a ba shi dama ya mulki Najeriya, musamman ma idan aka yi la’akari da irin gudunmawar da bai wa jam’iyyar wajen lashe manyan zabubbukan da suka gabata.