✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Tuchel zai raba gari da Bayern Munich a bazara

Mun yanke shawarar kawo ƙarshen alaƙarmu ta aiki a bazara bisa yarjejeniyar da muka amince da ita.

Kocin Bayern Munich, Thomas Tuchel, zai bar kungiyar a karshen wannan kakar wasannin shekara ɗaya kafin kwantiraginsa ya ƙare.

Bayanai sun ce zai raba gari da ƙungiyar ne sakamakon kashi da ta sha sau uku a jere, lamarin da ya sa ake hasashen cewa za ta ƙare kakar bana ba tare da ɗaukar kofi ko ɗaya ba.

Bayern ta ce an yanke shawarar sallamar Tuchel ne bayan ya tattauna da shugaban ƙungiyar Jan-Christian Dreesen dangane da sauye-sauyen da take yi.

“A tattaunawar ƙeƙe-da-ƙeƙe da aka yi, mun yanke shawarar kawo ƙarshen alaƙarmu ta aiki a bazara bisa yarjejeniyar da duka ɓangarorin muka amince da ita,” a cewar wata sanarwar da ƙungiyar ta ambato Dreesen yana bayyanawa.

“Babban burinmu shi ne mu samu sabon tsarin ƙwallon ƙafa wanda sabon koci zai jagoranta a kakar 2024-25.”

Tuchel ne ya jagoranci Bayern a nasarar lashe kofin Bundesliga a kakar bara bayan ya karɓi ragarmar gudanar da ita a bazara, amma a halin yanzu ƙungiyar tana bayan Bayern Leverkusen da tazarar maki takwas.

Ɗaya daga cikin wasannin ne inda Leverkusen ta doke ta da ci uku da nema – kuma Lazio ta doke Bayern Munich da ci ɗaya da nema a wasansu na farko a zagaye na sili-ɗaya-ƙwale na zagayen ’yan 16 a gasar Zakarun Turai.

Tsohon kociyan na Chelsea mai shekaru 50 ya maye gurbin Julian Nagelsmann ne a watan Maris din 2023, inda ya ƙulla yarjejeniyar har zuwa watan Yunin 2025.