✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Yadda ’yan bindigar Katsina suka mika makamansu

Ado da yaransa na daga cikin masu addabar Kananan Hukumomin Safana da Batsari a jihar Katsina

Daya daga cikin jagororin ’yan bindigar da suka addabi Jihar Katsina, mai suna Ado Sarki, ya bayyana tubansa tare da mika wa gwamnati makamansa.

Ado da yaransa na daga cikin masu addabar Kananan Hukumomin Safana da Batsari, yankunan da hare-haren ’yan bindiga suka yi wa mummunar illa a Jihar.

Ado wanda ya jagoranci wadansu daga cikin yaransa wurin mika makaman, ya yi alkawarin cewa sun yi hannun riga da ayyukan ta’addanci, ko da a bakin ransu ne.

Ga dai abin da Adon ya ce a lokacin mika makaman ga Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar, CP Sanusi Buba.