✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Yajin aikin ASUU: Gwamnati ta umarci a gaggauta bude jami’o’i

Gwamnati ta ba da umarnin ne ta bakin NUC

Gwamnatin Tarayya ta umarci Shugabannin jami’o’in Najeriya da su gaggauta sake bude makarantunsu don dalibai su ci gaba da karatunsu.

Umarnin na kunshe ne a cikin wata wasika da Daraktan Kudi na Hukumar Kula da Jami’o’i ta Kasa (NUC), Sam Onazi, ya fitar a madadin shugaban NUC, Farfesa Abubakar Rasheed ranar Litinin.

Jaridar Punch ta rawaito cewa wasikar wacce aka aike wa dukkan shugabannin makarantun Gwamnatin Tarayya da iyayen jami’o’in da ma hukumomin gudanarwarsu ta ce ya zama dole a sake bude makarantun.

“Ku tabbatar mambobin ASUU sun dawo kuma sun fara gudanar da lakca tare da dawo da harkokin yau da kullum a cikin jami’o’in,” kamar yadda wani bangare na wasikar yake cewa.

A ranar Larabar da ta gabata ce dai Kotun Ma’aikata ta umarci Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Kasa (ASUU) ta janye yajin aikinta, kodayake daga bisani kungiyar ta daukaka kara.

Tun a watan Fabrairun wannan shekarar ne dai malaman jami’o’in suka tsunduma yajin aikin tare da shan alwashin cewa ba za su koma ba har sai gwamnati ta cika musu alkawuransu.