Kungiyar al’ummar Arewa (CNG) ta sake kira ga jama’ar yankin da su tashi su kare kansu daga ’yan ta’adda.
CNG ta yi kiran ne bayan kisan da Boko Haram ta yi wa wasu manoma a garin Zabarmari da ke Karamar Hukumar Jere a Jihar Borno.
- Manoma 110 ne aka kashe a Zabarmari —MDD
- Arewa ta fi ko’ina hatsari a Najeriya —Sarkin Musulmi
- Kisan Borno: Sojoji sun musanta rahoton MDD
Kakakin kungiyar, Abdul-Azeez Suleiman, ya ce ba za a sake dogaro da dakarun Gwamnatin Tarayya don kare al’ummomin Arewa ba.
Suleiman, wanda ya ce halin da ake ciki yanzu ba “abin jurewa ba ne”, ya bukaci a yi wa shugabancin sojojin kasar da dukkan kadarorin tsaro garambawul nan take.