✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan bindiga sun sace basarake da wasu mutum 13 a Abuja

A cikin dare ’yan bindigar suka kutsa kauyen Chida da ke Karamar Hukumar Kwali suka sacw mutanen.

’Yan bindiga sun yi garkuwa da wani basarake tare da wasu mutum 13 a Yankin Babban Birnin Tarayya.

A cikin dare ne ’yan bindigar suka kutsa cikin kauyen Chida da ke Karamar Hukumar Kwali suka yi awon gaba da mutanen.

Wani dan unguwar mai suna Ishaya Musa, ya bayyana cewa maharan sun kuma harbi wani matashi mai shekara 18 da ya yi kokarin tserewa.

Ishaya Musa ya bayyana cewa a daren Juma’a maharan suka shigo suna harbi da bindigogi kirar AK-47 suka je kai-tsaye zuwa fadar basaraken suka dauke shi, kafin daga bisani su dauke sauran mutanen.

A cewar Ishaya, “Saboda firgita da karar harbe-harben, yaron ya yi kokarin tserewa, shi ne suka harbe shi a kafa, amma an kai shi asibiti.”

Sauran mutanen da aka dauke, suna kwakkwance ne a waje ne saboda tsananin zafi, lokacin da aka kai harin.

Ya ce a ranar Asabar da yamma jagoran ’yan bindigar ya kira iyalan wadanda aka sacen ya yi magana da su.

Kauyen Chida na da nisan kilomita uku daga Bukpe, kauyen da a bara ’yan bindiga suka sace basarakensa, Alhaji Hussaini Shamdozhi.

Bana kuma aka yi garkuwa da matarsa da ’ya’yansa uku a watan Fabrairu.