✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Za a fafata yakin basasa muddin aka kashe Gwamnan Binuwe – Wike

Akwai damuwa yadda rayuwar gwamnoni ke fuskantar barazana a Najeriya.

Gwamna Nyesom Wike na Jihar Ribas, ya sanar cewa muddin aka kashe takwaransa na Jihar Binuwe, Samuel Ortom, to kuwa alhakin jininsa zai rataya a wuyan Gwamnatin Tarayya.

A ranar Asabar da ta gabata ce aka kai wa gwamnan na Benuwe hari, inda wasu ’yan bindiga suka bude wa ayarin motocinsa hari a kan hanyar Makurdi zuwa Gboko da ke Karamar Hukumar Makurdi ta jihar.

A yayin da yake martani dangane da lamarin a Fatakwal, babban birnin jihar Ribas, Wike ya ce idan har aka kashe gwamnan Benuwe, to akwai yiwuwar a sake fafata wani yakin basasa a kasar nan.

A cewarsa, “Idan kun kashe Ortom, to ku shirya yi wa Najeriya jana’iza. Don muddin wani abu ya sami Gwamna Ortom, alhakinsa zai rataya a wuyan Gwamnatin Tarayya ne kuma ta tabbata ta zauna cikin shiri don Najeriya za ta gushe daga kasancewa.”

Wike ya kuma yi zargin cewa a lokacin babban zaben kasa na 2019, tsohon Kwamandan rundunar sojin kasa a shiyar Fatakwal, Manjo Janar Jamil Sarham da kuma wasu kusoshin jam’iyyar APC sun kammala shirin kawar da shi daga doron kasa.

Ya bayyana damuwa a kan lamarin yadda rayuwar gwamnoni ke ci gaba da fuskantar barazana ya zama ruwan dare a kasar nan.