✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Buhari zai sake bai wa su Buratai mukami

Shugaba Muhammadu Buhari ya nemi Majalisar Dattawa ta amince da nadin.

Shugaba Muhammadu Buhari ya nemi Majalisar Dattawa ta amince da nadin tsaffin manyan hafsoshin soji da ya sallama a makon jiya a matsayin jakadun Najeriya.

Sanarwar hakan tana kunshe cikin wani sako da hadimin shugaban  kasar na shafukan sada zumunta, Bashir Ahmad ya wallafa da Yammacin ranar Alhamis a shafinsa na Twitter.

Hadimin shugaban kasar ya ce an aike da sunayen tsaffin manyan hafsoshin sojin da suka yi ritaya zuwa Majalisar Dattawan Najeriya da zummar nada su a matsayin jakadu ga kasar a wasu kasashe na ketare.

Malam Bashir ya ce tsaffin manyan hafsoshin sojin da da aka aike wa Majalisar Dattawan sunayensu sun hadar da Janar Abayomi Olanisakin da Vice Admiral Ibok-Ete Ibas.

Sauran sune Laftanar Janar Tukur Buratai da Air Marshal Sadique Abubakar da kuma Air Vice Marshal Muhammad S Usman.