✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Fashewar Gurneti ta hallaka yara 5 a Borno

Biyu daga cikin yaran sun mutu nan take, uku kuma a asibiti.

Akalla yara biyar sun mutu bayan wani Gurneti da suke wasa da shi ya tarawatse a garin Ngala na Jihar Borno.

Lamarin dai ya faru ne ranar Alhamis a garin da ke dab da kan iyakar Najeriya da kasar Kamaru, kamar yadda wani dan sa-kai a yankin ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labaran Faransa na AFP.

“Yaran su biyar sun dauko Gurnetin ne lokacin da suke kiwo a wajen garin, inda ya fashe a hannunsu, lokacin da suke wasa da shi,” inji Umar Kachalla, wani dan sa-kai a yankin.

“Biyu daga cikinsu sun mutu ne nan take, ragowar ukun kuma sun mutu a asibitin Mada, da ke kasar Kamaru.” inji shi.

Kazalika, shi ma wani dan aikin sa-kan, Umar Ari ya bayar da makamancin wannan bayanin inda ya ce lamarin ya faru ne ranar Alhamis.

Ari ya ce har yanzu burbushin Gurneti na ci gaba da yin barna a yankin, musamman a kan yara kanana wadanda ko dai suke mutuwa ko kuma su jikkata.

A watan Agustan 2014, mayakan kungiyar Boko Haram sun taba kwace iko da garin na Ngala da na Gamboru da ke da makwabtaka da shi.

Sai dai a shekarar 2015, sojojin Najeriya da gudunmawar na Chadi sun kwato garuruwan Bayan kwashe watanni suna kai hare-hare.

Ko a watan Disamban 2019, mutum tara sun mutu, 26 kuma sun jikkata lokacin da wani abin fashewa ya tashi a wata gada mai cike da cunkoso da ta hada garuruwan Gamboru da Fotokol.

Mazauna yankunan dai sun yi zargin cewa ’yan ta’addan Boko Haram ne suke ba yaran kyautar Gurnetin a matsayin kayan wasa. (AFP)