✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Hotuna: Ganduje ya kai wa Buhari zanen gadar da zai gina a birnin Kano

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na Jihar Kano, ya ziyarci Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a fadarsa ta Villa da ke birnin Abuja. Gwamna Ganduje da Yammacin…

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na Jihar Kano, ya ziyarci Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a fadarsa ta Villa da ke birnin Abuja.

Gwamna Ganduje da Yammacin ranar Litinin ya gabatar wa Shugaban Kasar zanen gadar da yake shirin ginawa a birnin Kano wacce tuni an sanya mata suna ‘Gadar Muhammadu Buhari’.

Ana sa ran fara ginin sabuwar gadar mai hawa uku a kan titin Hotoro a shataletalen gidan man NNPC da ke Karamar Hukumar Tarauni.

Buhari yayi duba zanen sabuwar gadar
Ganduje yayin da yake mika wa Buhari zanen gadar
Ganduje yayin gaisawa da Shugaba Buhari
Buhari yayin zantawa da Gwamna Ganduje