Ana fargabar wasu ’yan bindiga sun kashe wani matashi mai suna Sabo Yusuf a yankin Kawo na Jihar Jigawa.
Zahraddeen Aminuddeen wanda ke zaman Kakakin rundunar ’yan sandan jihar shi ne ya inganta rahoton kamar yadda manema labarai na BBC suka ruwaito.
- PDP za ta yi watsi da tsarin karba-karba a 2023
- Ba sace ni aka yi ba, guduwa na yi – Amaryar Kano
- ’Yan bindiga: Sheikh Gumi yana mana katsalandan – Masari
A cewarsa, maharan sun kai hari gidansu Sabo da tsakar daren Laraba, inda suka yi awon gaba da mahaifiyarsa da kuma wani dan uwansa.
Kakakin ya ce Sabo ya rasu ne a wani Asibitin Birnin Kudu da aka garzaya da shi bayan maharan sun harbe shi a kirji.
“Da misalin karfe 3:35 na daren Laraba ne ’yan sandan Birnin Kudu suka samu rahoton cewa wasu ’yan bindiga sun far wa gidan Alhaji Abubakar mai shekara 50 a Kawo.”
“Sun harbi dansa a kirji mai suna Sabo Yusuf dan shekara 25,” a cewar Kakakin.
Ya kara da cewa, a halin yanzu dai Kwamishinan ’yan sandan jihar ya tura jami’ai rundunar yaki da maki zuwa yankin.