✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Rikicin Ukraine: Gwamnatin Tarayya za ta gaggauta dawo da ’yan Najeriya gida

Za a soma kwaso 'yan Najeriya daga yankunan da suka hada da Donestk da Luhensk.

Gwamnatin Tarayya ta sanar da aniyarta na soma dawo da ’yan Najeriya gida daga kasar Ukraine biyo bayan mamayar da Rasha ta yi wa kasar.

Gwamnati ta dauki azamar gudanar da wata jigilar jiragen sama ta musamman domin kwaso yan kasarta daga Ukraine sakamakon yadda rikici ke kara ta’azzara tsakanin kasar da Rasha.

Ministan Harkokin Wajen Kasar, Geoffery Onyeama a wata hirarsa da gidan talabijin na NTA, ya ce an tuntubi Ofishin Jakadancin Najeriya da ke Kiev domin soma jigilar wadanda ke son dawowa gida Najeriya.

Ministan ya ce ma’aikatarsa na ci gaba da bibiyar duk abin da ke wakana a kasar ta Ukraine tare da shan alwashin cewa za a yi duk wata mai yiwuwa wajen bai wa ’yan kasar kariya musamman dalibai.

A ranar Alhamis ce dai Shugaban Majalisar Wakilai, Femi Gbajabiamila ya umarci Shugaban Masu Rinjaye na majalisar da ya gaggauta tattaunawa da Ma’aikatar Harkokin Wwajen Najeriya domin shirya yadda za a dawo da ’yan Najeriya daga kasar Ukraine da Rasha ta mamaye.

Gbajabiamila ya umarci Ado Doguwa ya tattauna da Shugaban Kamfanin Jiragen Saman Najeriya na Peace Air domin shirya yadda za a dawo da ’yan Najeriya gida.

Kasar Rasha ta mamaye wasu sassa na kasar Ukraine tun daga ranar Alhamis inda ta rika yi wa kasar luguden wuta ta sama bayan ta aika da sama da sojojinta 200,000 zuwa iyakan kasar da manyamanyan tankokin yaki

A rahotanni da ke bayyana daga kasar Ukraine an rika ganin yadda rugugin wuta na nakiyoyi da igwa igwa ta sama da kasa da sojojin kasar Rasha ke aikawa kasar Ukraine din.

Gwamnatocin kasashe da dama sun yi tofin Allah-Tsine ga wannan hare-hare na sojojin Rasha a kan kasar Ukraine.

Kasashen duniya ciki har da Amurka, Birtaniya, Faransa da sauran manya-manyan kasahen duniya na gargadin Rasha ta shiga taitayinta sannan sun bayyana cewa lallai za su saka wa kasar takunkumi masu tsauri da zai yi lagalaga da tattalin arzikin kasar.

Zuwa yanzu farashin danyen man fetur ya yi tashin gwauron zabi a dalilin wannan mamaya da Rasha ta kaiwa Ukraine.

Tarayyar Turai ta kakaba wa Rasha takunkumi

Kungiyar Tarayyar Turai (EU) ta kakaba tunkumin karya tattalin arzikin  kasar Rasha, bayan dakarun Rasha sun kaddamar da hare-hare a kan kasar Ukraine.

A safiyar Alhamis EU ta bukaci Rasha ta gaggauta janye sojojinta da matakin sojin da ta dauka a kan Ukraine, sannan ta sanar da wasu karin matakan karya tattalin arzikin Rasha da kasashen EU za su dauka.

Shugabar Hukumar EU, Ursula von der Leyen, ta ce, matakan, “Za su shafi muhimman bangarorin tattalin arzikin Rasha, ta hanyar katse su daga ci gaban zamani da manyan kasuwanni mau muhimmanci ga Rasha.

Za mu gurgunta cibiyar tattalin arzikin Rasha tare da hana ta damar tafiya da zamani; Za mu kwace kadarorin Rasha da ke kasashen EU, tare da katse huldar bankunan kasar da kasuwar hada-hadar kudaden Tarayyar Turai.

“Kamar yadda muka dauki matakin a baya, har yanzu muna tare da kasashen Amurka, Birtaniya, Kanada, da kuma Japan da Australiya da sauransu a kan wanna batu.”

Matakan na zuwa ne bayan Shugaban Rasha, Vladimir Putin ya umarci dakarun kasarsa da su ragargaji yankunan Ukraine da suka kutsa, yadda ya kamata.

Hotuna hare-haren da sojojin Rasha suka kai ya nuna yadda aka ragargaza gine-gine, a yayin da wasu majiyoyi ke cewa an kashe fararen hula 10 da sojoji da dama.

Tuni dai gwamnatin ta dakatar da zirga-zirgar jiyage a Yammacin kasar da ke makwabtaka da Ukraine.

Putin dai ya musanta cewa yaki ya kaddamar a kan Ukraine, yana mai kiran abin da sojojinsa ke yi da cewa wani ‘aikin soji ne na musamman.’

Putin dai na goyon bayan yankunan Doniestk da Dombass da ke neman ballewa daga Ukraine.

Shugabar Hukumar EU, Ursula von der Leyen, ta ce, miliyoyin al’ummar Rasha ba sa goyon bayan komar da hannun agogo baya da Putin yake son yi, sannan EU da al’ummar kasashen EU na tare da mutanen Ukraine kai da fata.