✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

ASUU za ta bude jami’o’i a watan Janairu 2021 —Minista

Ranar Talata Gwamnati da malaman jami'a za su tattauna kan janye yajin aikin

Ministan Kwadago da Samar da Ayyuka, Chris Ngige ya bayar da tabbaci cewa Kungiyar Malaman Jami’a (ASUU) za ta janye yajin aikin da take yi a watan Janairun 2021 mai kamawa.

Ngige ya kara da cewa Gwamnatin Tarayya riga ta biya kusa dukkannin bukatun malaman jami’a, saura dan abin da bai taka kara ya karya ba.

“Mun biya kashi 98 cikin 100 na bukatun ASUU; kashi 2 cikin 100 da ya rage kuma shi ne ake alkawari.

“Ina kyautata zaton zuwa karfe 12 na dare ranar Litinin akwai ayyukan da za mu yi; su ma da wanda za su yi a bagarensu”, inji Ministan Ilimin.

Ya ce bangaren gwamnati da ASUU za su tattauna kan ragowar kashi biyun bukatun malaman a zaman da bangarorin za su yi ranar Talata.

Ya ce bayan tattaunawar ana sa ran ASUU ta janye yajin aikinta a ci gaba da karatu a jami’o’i a watan Janairun 2021.

“Ranar Talata za mu tattauna, mu kuma hada abin da muke da shi da wadanda suke da shi na bayanai; na tabbata da zarar mun tattauna maganar yajin aiki ta kare,” inji Ngige.

A watan Maris ne malaman jami’a karkashin kungiyar ASUU suka fara yajin aiki domin neman biyan bukatunsu.

Bukatunsu sun hada da soke batun sanya su a tsarin albashi IPPIS na bai-daya da Gwamnatin Tarayya ta bullo da shi; biyan alawus din da suke bin bashi; da kuma samar wa jami’o’i wadatattu kudade da sauransu.